Surah At-Tin ( The Fig )

Hausa

Surah At-Tin ( The Fig ) - Aya count 8

بِّسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيْتُونِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.

وَطُورِ سِينِينَ ﴿٢﴾

Da Dũr Sĩnĩna.

وَهَٰذَا ٱلْبَلَدِ ٱلْأَمِينِ ﴿٣﴾

Da wannan gari amintacce.

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَٰنَ فِىٓ أَحْسَنِ تَقْوِيمٍۢ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.

ثُمَّ رَدَدْنَٰهُ أَسْفَلَ سَٰفِلِينَ ﴿٥﴾

Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۢ ﴿٦﴾

Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِٱلدِّينِ ﴿٧﴾

To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?

أَلَيْسَ ٱللَّهُ بِأَحْكَمِ ٱلْحَٰكِمِينَ ﴿٨﴾

Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?