Surah Az-Zalzalah ( The Earthquake )

Hausa

Surah Az-Zalzalah ( The Earthquake ) - Aya count 8

إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا ﴿١﴾

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا ﴿٢﴾

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

وَقَالَ ٱلْإِنسَٰنُ مَا لَهَا ﴿٣﴾

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا ﴿٤﴾

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا ﴿٥﴾

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْاْ أَعْمَٰلَهُمْ ﴿٦﴾

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ ﴿٧﴾

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ ﴿٨﴾

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.